Buhari yaba yan Najeriya tabbacin samun tsayayan wutar lantarki
– Shugaban kasa Muhammadu Buhari yace kasar Najeriya na da dukkan abubuwa biyu na albarkatu da fasahar da zata cimma bayar da tsayayyen wutar lantarki
– Yace tare da ingantattun wutan lantarki, ayyukan Najeriya zata samu ci gaba
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba yan’Najeriya tabbacin cewa gwamnatinsa tana aiki don gannin ta shawo kan matsalar wutar lantarki da ke addabar kasar. Jaridar Leadership ta ruwaito cewa shugaban kasa Buhari ya bada tabbacin a wani taro tare da shugaban kasar Togo, Faure Gnassingbe da ya kawo ziyara, a fadar shugaban kasa dake babban birnin tarayya Abuja a ranar Talata, 2 ga watan Augusta.
Ya bayyana cewa kasar Najeriya tana da albarkatun da fasahar da zata cimma manufarta.
KU KARANTA KUMA: Sojoji sun kashe yan Boko Haram 5 a jihar Borno
Tribune ta ruwaito cewa Buhari ya kuma bayyana cewa shugabannin biyu sun kuma tattauna lamarin a kasar kudancin Sudan da Kasar Burundi. Yana fatan cewa taron kungiyar tarayyar Afrika wato African Union (AU) zai taimaka gurin daidaita dattakon lamarin a kudancin Sudan da kasar Burundi a kokarin da ake yi.
A bangarensa, Gnassingbe ya kuma gayyaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya halarci taron maritime da za’ayi a Kasar Togo cikin watan Oktoba na wannan shekarar. A halin yanzu shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi tankade da rairaya da dama a ma’aikatar tarayya tare da nada Enikanolaiye, Audu-Rafiu Olusola a matsayin sakatariya da kuma sake wa sakatarorin tarayya takwas (8) guri.
The post Buhari yaba yan Najeriya tabbacin samun tsayayan wutar lantarki appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.