Minista ta bayyana makudan kudaden da gwamnati ke tatalawa
Ministan kudi ta Najeriya Kemi Adeosun ta bayyana cewa gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaba Buhari na tattalin makudan kudade duk wata.
Kemi Adeosun tana bayani akan tattalin arzikin kasa.
Ministan ta bayyana hakan ne yayi da take tattaunawa da wasu yan majalisun tarayya. Ministan tace gwamnatin Najeriya tana tattala N6b a duk wata daga kudaden albashi da gudanarwar gwamnati sakamakon yanyoyin da gwamnatin ta bullo da su don tsuke bakin aljihu.
Ministan har ila yau ta shaidawa yan majalisun cewa gwamnati ta bullo da wadannnan dubarun na tattali ne da nufi rage kudaden da ake kashewa musamman ma yanzu da darajar mai na ragu sosai. A cewar ta: “Gwamnatin tarayya yanzu tana kashe N159b a duk wata maimakon N165b da ake kashewa a watannin baya wajen ayyukan gudanarwa kawai.”
Mai karatu zai iya tunawa cewa yan majalisar kasar nan dai sun aike da takardar sammaci zuwa ga ministan a cikin watan Mayun da ya gabata domin ta bada ba’asin yanayin kundin kasafin kasar da ma sauran abubuwa amma sai bata samu dama ba.
A wancen lokacin ne ma ministan ta bada uzurin cewa bazata iya zuwa amma sai yan majalisar dattijan suka bukaci ta tabbata ta bayyana a gaban ta kafin tafiyar su hutu.
The post Minista ta bayyana makudan kudaden da gwamnati ke tatalawa appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.