– Dan majalisar wakillai daga jihar Kano wanda kuma yanzu haka aka kora saboda takaddamar dake tsakanin sa na shugaban majalisar Abdulmumin Jibrin ya bayar da satar ansar cewa zai fa iya tsayawa takarar shugaban kasar Najeriya a zabe mai zuwa a shekara ta 2019
– Dan majalisar wanda yanzu haka yake a matsayin korarre yana wakiltar mazabar Kiru da Bebeji ne daga jihar Kano
Dan majalisar ya bayar da satar ansar zai iya tsayawa takarar ne ta hanyar akawut din sa na Tuwita a yau din nan Talata 22 ga watan Nuwamba.
KU KARANTA: INEC ta watsa wa PDP kasa a ido
Ga yadda ya rubuta nan da harshen turanci:
A saman ya rubuta cewa shugaba Muhammadu fa ba barawo bane kuma ba ruwan sa da cin hanci da rashawa. Zan kuma sake zaben sa a zabe mai zuwa sai dai kuwa idan nima ina takarar.
A jiya dai ne muka ruwaito maku cewa Kwanakin baya ne lokacin rikicin cogen da aka ce ‘yan majalisa sun yiwa kasafin kudin bana Abdulmummuni Jibrin ya fito ya zargi majalisa da yin magudi lamarin da ya sa suka dakatar dashi har na tsawon kwanaki 180.
A karshen makon da ya gabata ne wasu mutane su 29 suka wakilci al’ummar kananan hukumomin Kiru da Bebeji wajen kai majalisar wakilan Najeriya kara kotu akan dakatar da mai wakiltarsu Onarebul Abdulmummuni Jibrin.
Barrister Muhammad Bashir Muntaka shi ne lauyan al’ummar. Yace mutanen da suka zabi Abdulmummuni Jibrin sun gaji da zama basu da wakilci a majalisar. Mutanen suna ganin dakatar da dan majalisar har na tsawon kwanaki 180 an sabawa ka’ida.Inji Barrister Muntaka babu wata doka da ta baiwa majalisar ikon dakatar da wani dan majalisar fiye da kwanaki 14. Babu wata doka da ta amince da kwanaki fiye da haka.
Hakazalika Barrister Muntaka ya fayyace abubuwan da al’ummar Kiru da Bebeji ke bukata daga kotun. Suna son kotun tace dakatarwar da aka yiwa Abulmummuni Jibrin bata kan ka’ida. Kotu kuma ta biyashi kudi da hakkin da aka tauye masa na kwanakin da aka dakatar dashi.
A biyo mu a shafin mu na Tuwita @naijcomhausa
The post Abdulmumin Jibrin zai nemi takarar shugaban kasa a 2019 appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.