Добавить новость


World News in Dutch


Новости сегодня

Новости от TheMoneytizer

Trump: Wasu yan Najeriya da suka kama kasa a Amurka

Alkawarin shugaba mai jiran gado na Amurka Donald Trump na korar ‘yan Afrika mazauna Amurka da zaran ya ci zabe ba sabon labrai ba ne, sai dai da akwai wasu yan Najeriya da sabon shugaban bai isa ya koresu ba soboda sun kama kasa

Trump ko ina alkawarinsa na korara baki ‘yan Africa?

Jude O Nkama: Dan Najeriya kuma dan Afrika na farko da a ranar 6 ga watan Janairu aka nada shi  a mukamin mai Shari’a a tarihin shekaru 349 na birnin New Jersey . Zai yi wahala Trump ya iza keyarsa gida.

Hakeem, Kae-Kazim: Fitaccen mai fitowa a fina-finai ne, a kadan daga cikinsu shi ne wasan talbijin na Starz na Black Sails  da kuma fitowarsa a matsayin George Ratanga a fim din Hotel Rwanda na Shekarar 2004. Baya ga wannan dan asalin Najeriyar shine jakadan kungiyar mai zaman kanta ta Africa 2.0 wacce ke da rajin ganin an samar da ingantaccen jagorancin a nahiyar Africa.

Wale: cikakken sunansa shi ne Olubowale Victor Akintimehin da aka Haifa a shekara 1984, asalinsa dan Najeriya ne, kuma ya yi suna a wake-waken zamani salon Rapp. Tauraruwarsa ta haska ne a shekara 2006, bayan wata waka da ya yi mai suna Dig dug” (Shake it).

Wale yayi fice matuka a inda ya fito a shiryen gidajen talbijin daban-daban na kasa ciki har da MTV da sauran wasu manya-manyan jaridu na bakaken fata.

KU KARANTA KUMA: Hanyoyi 6 da mulkin Trump zai taba rayuwar ‘yan Najeria

Uzo Aduba: Cikakken sunanta shi ne Uzoamaka Nwanneka “Uzo” wacce aka haifa a 1981, ‘yar wasan kwaikwayo ce, kuma mawakiya. Ta samu kyautuka na yabo daga irin wasannin da ta fito, iyayenta ‘yan asalin Achi ne daga jihar Enugu.

Samuel Ifeanyi : Dan asalin jihar Legas ne, mahaifinsa dan Najeriya, mahaifiyarsa kuma baamurkiya,  Dan siyasa ne, kuma dan jam’iyyar Democrat daga Indianapolis, Indiana. Yana daya daga cikin majalisar birnin Indianapolis daga gunduma ta 15 ta kudu maso yammaci, kuma tsakiyar birnin. A ranar 22 ga watan Disamba na shekarar 2011, mai shari’a na jihar ya ayyana shi a mukamin  magatakardar jihar.

Kadan ne daga cikin ‘yan Najeriya masu rike da muhimman matsayi da kuma mukamai wanda kasar Amurka ke amfana da su matuka, wanda zai yi wuya sabon shugaban ya iza keyarsu zuwa gida.

The post Trump: Wasu yan Najeriya da suka kama kasa a Amurka appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.

Читайте на сайте


Smi24.net — ежеминутные новости с ежедневным архивом. Только у нас — все главные новости дня без политической цензуры. Абсолютно все точки зрения, трезвая аналитика, цивилизованные споры и обсуждения без взаимных обвинений и оскорблений. Помните, что не у всех точка зрения совпадает с Вашей. Уважайте мнение других, даже если Вы отстаиваете свой взгляд и свою позицию. Мы не навязываем Вам своё видение, мы даём Вам срез событий дня без цензуры и без купюр. Новости, какие они есть —онлайн с поминутным архивом по всем городам и регионам России, Украины, Белоруссии и Абхазии. Smi24.net — живые новости в живом эфире! Быстрый поиск от Smi24.net — это не только возможность первым узнать, но и преимущество сообщить срочные новости мгновенно на любом языке мира и быть услышанным тут же. В любую минуту Вы можете добавить свою новость - здесь.




Новости от наших партнёров в Вашем городе

Ria.city
Музыкальные новости
Новости России
Экология в России и мире
Спорт в России и мире
Moscow.media










Топ новостей на этот час

Rss.plus