Rohr ya bukaci yan wasan Super Eagles su magance matsalar tsaron gida
Mai horar da kungiyar kwallon kafa ta kasa Super Eagles, Gernort Rohr yace ya zama dole yan wasan Super Eagles su gyara tsarin bayansu idan dai suna so samu shiga gasar cin kofin Duniya na shekarar 2018 a kasar Rasha.
Rohr ya bayyana haka ne bayan wasan da aka fafata tsakanin kasar Algeria da Najeriya, inda Najeriya ta lallasa Algeria da ci 3-1.
Rohr ya nuna damuwarsa game da yawan ire iren daman cin kwallaye da masu tsaron gidan suka kyale Riyad Mahrez, da Yacine Brahimi suka dinga samu bayan an dawo hutun rabin lokaci. Matsalar da muka fuskanta kawai itace damammakin da Algeriya suka samu a sashi na biyun wasan, inji Rohr.
KU KARANTA:Gayyar sodi tayi sanadiyyar mutuwar matashi
Nasan abune mai wuya rike yan wasan Algeria, amma yan wasan mu masu tsaron gida sun nuna kwarewa. Sai dai ya bayyana cewar dole sai mun sake zage damtse musamman a bangaren tsaron gida.
Mikel da Victor Moses bayan cin kwallon su
Rohr ya cigaba da bayanin matsalar da Najeriya ke dashi musamman ta bangaren lamba Uku.
Muna da yan wasa masu buga lamba uku, sunyi kokari, amma dole ne mu tantance tsayayyen wanda zai dinga buga mana. Amma naji dadin sakamakon wasan.
A wasan daya gudana a filin wasa na garin Uyo, yan wasan Chelsea Moses Victor da Mikel Obi ne suka zura kwallaye Uku, inda dan wasan Algeria Nabil Bentaleb ya zura kwallo guda, hakan ya baiwa kasar Najeriya maki uku.
The post Rohr ya bukaci yan wasan Super Eagles su magance matsalar tsaron gida appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.