Ana zargin jami’an tsaron Najeriya da wannan aika-aikar
– Kungiyoyin kare hakkokin bil adama na zargin sojojin Nageriya da ‘yansanda da cewa suna kuntatawa mutanen dake samun kubuta daga hannun mayakan Boko Haram, ciki harda wadanda suke yiwa fyade
– Yayinda mutanen ke zaton cewa in sun shiga hannun ma’aikatan tsaron, sun kubuta daga ukubar.
The policeman being beaten by the angry mob
A cikin wata kasida mai shafuna 12 da ta gabatar jiya, kungiyar kare hakkin bil adama ta Human Rights Watch ta bada misalin abinda ya sami wasu mata 43 da aka ajiye a wasu daga cikin sansanonin ‘yan gudun hijira guda 7 dake Maiduguri, hedkwatar jihar Borno kuma inda daga nan ne kungiyar Boko-Haram ta samo asali a shekarar 2009.
Hudu daga cikin matan sunce manyan jami’an dake kula da wadanan sansanonin sun bugar da su da ababen sa maye kana suka yi musu fyade, yayinda mata 37 kuma suka ce an zambace su an kwana da su bayanda aka yi musu alkawarin bogi na cewa za’a agaza musu da wasu kaya ko ma za’a aure su.
Rahoton yace da yawa daga cikin matan an watsar da su bayanda suka dauki ciki.
Izuwa yanzu dai hukumomin gwamnatin ta Nigeria basu maido da wani martani kan wannan zargin ba.
A wani labarin mai kama da wannan kuma Bincike ya nuna cewa hukumar EFCC na tuhumar sabon sirikin shugaban kasa Muhammadu Buhari, wato Ya’u Gimba Kumo kan wasu naira bilyan 3 da suka salwanta a lokacin da yake manajan darakta na bankin FMBN, kamar yadda majiyarmu ta Sahara Reporters ta rawaito
Shi dai Ya’u Kumo shine aka daura aurensa da ‘yar shugaba Buhari mai suna Fatima a makon da ya gabata a garin Daura.
https://youtu.be/nT0m4FpgP-w
The post Ana zargin jami’an tsaron Najeriya da wannan aika-aikar appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.