An kama wani mai gadi yayi sata
– Kotu a Abuja ta kama wani mai gadi yayi sata, kuma kotun da ke unguwar Area I a birnin tarayya ta bada belin wanda ake zargi
– Ana zargin wannan mai gadin ya sace kayan gini
Wani Kotu da ke zama a Unguwar Karmo da ke Area 1 a Babban Birnin Tarayya Abuja, ta bada belin wani saurayi da ake zargi da laifin yayi sata. Ana zargin wannan saurayi da bai wuce shekaru 19 ba ya sace kayan ginin gidan da yake gadi a Garin na Abuja.
Alkalin Kotun na Area 1, Abubakar Sadiq ya bada belin wannan mai gadi mai suna Peter Gwaza Inji Jaridar Daily Trust. An bada belin na sa ne a kan kudi har N500,000 tare da kawo wanda zai tsaya masa.
KU KARANTA: Babbar mota ta kashe ‘yan makaranta
Kotun tace dole wanda zai tsayawa wannan mai gadi da ake zargi da lafin sata ya zama ma’aikacin Gwamnati, kuma wanda yake akalla mataki na 7 na aiki. Yanzu haka dai an daga shari’ar zuwa 10 ga wannan wata. An bayyana cewa dai wanda ake zargi ya bayyana cewa ya saci kayan da ake magana, har ma ya sayar da su tuni kan kudi N17,000.
Zannah Dalhatu, wanda ke karar wannan saurayi yace, Peter Gwaza ya kasance mai masa gadin gidan sa da ke Daki Biyu, ko da ya zo wani lokaci sai ya ga cewa an sace masa kayan gini, Nan take ya ruga wurin ‘Yan Sanda.
The post An kama wani mai gadi yayi sata appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.