Abubakar Usman ya kashe mahaifiyarsa, ya daura laifin kan mahaifin sa
-Abubakar Usman yayi da’awar cewa mahaifin sa yayi masa sihiri somin ya kashe mahaifiyar sa
-Makiyayin ya nace kan cewa baiyi niyan aikata kisa ba
-Ya kuma soki matar dan’uwan sa
Jami’an yan sanda sun kama Abubakar Usman wanda ya kasance Fulani makiyayi, bayan ya soki mahaifiyar sa da matar dan’uwansa har lahira
Jaridar Punch ta ruwaito cewa makiyayin mai shekaru 25 a duniya ya kashe mahaifiyarsa da ta manyanta Khadijat da kuma Ramatu Shagari wacce ta kasance matar dan’uwansa. Jami’an yan sandan jihar Kwara sun tisa keyar Usman a ranar Laraba, 24 ga watan Augusta a garin Ilorin babban birnin jihar Kwara.
Duk da haka, mai laifin yace shi baiyi niyan aikata kisan kai ba kuma ya daura laifin a kan mahaifinsa wadda yayi zargin cewa yayi mai sihiri ne.
KU KARANTA KUMA: CAN ta maida martani kan kisan Kiristoci
“Ina cikin aikin kiwo. A ranar lokacin da na tashi daga bacci, Na dauki naira 1000 daga dakina sannan na dauki shanayena domin kiwo. Nan da nan, sai na lura da cewa dabbobina suna guduwa sai na bi su. A lokacin da na koma gida, wani abu ya shige ni sai na soki mahaifiyata da wuka. Na kuma soki matar yayana. Na yarda da cewan mahaifina ne yayi mun sihiri. Bana da ciwon hauka.”
The post Abubakar Usman ya kashe mahaifiyarsa, ya daura laifin kan mahaifin sa appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.