APC ta dakatad da zaben fidda gwani a Jihar Ondo
– An jinkirta zaben fidda gwanin jam’iyyar APC a takaran gwamnan Jihar Ondo
– An dakatad da shi zuwa karshen wata
Jam’iyyar APC shiyar Jihar Ondo ta dakatad da zaben gidsa gwani na takaran gwamnan jihar Ondo da aka shirya yi a ranar 27 ga wata. Sakataren hulda da jama’a na jam’iyyar ya alanta hakan ne a wata jawabin da ya saki a ranan laraba, 24 ga watan agusta a birnin Akure.
kakaki ilori
Jawabin tace : “An yanke wannan shawara ne a karshen ganawar gaggawan da kwamitin aikin jam’iyyar ta kasa ta a ranan 24 ga watan Agusta. An dakatad da zaben zuwa laraba, 31 ga watan agusta saboda dalilin kayan aiki.”
Za ku tuna cewa an samu rahotanni cewa za’a yi zaben share faggen ne a barikin Soji da ke Jihar Ondo saboda tsoron masu tada tarzoma.
A bangare guda, an samu rashin jituwa tsakanin mambobin jam’iyyar,yayinda suka fara fada da juna bayan an zargi shugaban jam’iyyar da kasancewa dan lekan asiri, rufa rufan deligat da kuma yunkurin taimaka wa wani dan takara a zaben fidda gwanin.
KU KARANTA : Shugaba Buhari ya gana da majalisar ministocinsa
A wata labarin, tsohon kwamishanan shari’a kuma babban lauyan Jihar Ondo ,Eyitayo Jegede, ya lashe zaben fidda gwanin jam’iyyar PDP a zaben takaran gwamnan Jihar ta Ondo.
The post APC ta dakatad da zaben fidda gwani a Jihar Ondo appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.