An kashe wasu mutane biyar da ake zargin yan kungiyar asiri ne ta ‘Aye’ a yayin wata fafatawa da suka yi da wata kungiyar hamayyarsu a yankin Sagamu na jihar Ogun. Hatsaniyar ta afku ne tsakanin kungiyoyin asirin a ranar talata 2 ga watan agusta zuwa ranar laraba 3 ga watan agusta inda suka yi […]
The post Al’ummar Ogun sun tsere bayan mutuwar mutane 5 a hatsaniya appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.
An kashe wasu mutane biyar da ake zargin yan kungiyar asiri ne ta ‘Aye’ a yayin wata fafatawa da suka yi da wata kungiyar hamayyarsu a yankin Sagamu na jihar Ogun.
Hatsaniyar ta afku ne tsakanin kungiyoyin asirin a ranar talata 2 ga watan agusta zuwa ranar laraba 3 ga watan agusta inda suka yi amfani da munanan makamai.
News Telegraph ta ruwaito cewa mutane uku yan kungiyar Aye ne suka rasa rayukansu, inda su kuma abokan hamayyar tasu suka rasa mutane biyu a yayin rama biki da sukayi a ranar laraba. A cewar wani majiyarmu da aka yi a gabansa, yace duk al’ummar yankin sun tsere daga garin.
Yace “kungiyoyin asirin da basa ga maciji da juna sun shirya gudanar da bikin kaddamar da sababbin mambobinsu ne a ranakun 7 da 8 ga watan agusta. “zuwa yanzu dai bamu sani ko matsalar ranaku ne ta kawo rikicin ba.” Rahotanni sun nuna cewa al’ummar yankin sun koka kan rashin zuwan yansanda unguwar tun ranar farko da aka fara rikicin.
A wani labarin makamancin wannan, mutum daya ya rasa ransa a jihar Delta bayan wata rikici da ta afku tsakanin kungiyoyin asiri na hamayya. Rikicin ya faru ne a kauyen Obiaruku na karamar hukumar Ukwuani dake jihar Delta. Rikicin na hamayya ya faru ne a ranar talata 12 ga watan yulio.
The post Al’ummar Ogun sun tsere bayan mutuwar mutane 5 a hatsaniya appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read Naij.com 24/7.