Matar Kanu ta soki shugaba Buhari
-Tayi bayani kan zargin cewa mijinta zai bar fafutukar ‘yancin Biafra
-Ta bayyana tsare kanu a matsayin zalunci da rashin adalci
-Ms Kanu tayi kira ga shugaba Buhari da ya sa Kanu cikin tattaunawar da ake yi da Neja Delta Avengers
Uchechi Okwu-Kanu, matar Dan rajin Biafra ta maida martani game da zancen da ake cewa maigidanta Namdi Kanu yayi watsi da maganar Biafra. A wata hira da tayi da IBTimes UK ta karyata cewa mijinta ya hakura da neman ‘yanci, tana cewa zargin da ake ma kanu ba gaskiya bane kuma cin fuska ne. Ta ci ga a da cewa ” duk Wanda ke tunanin mijina zai watsi da Biafra, to mahaukaci ne”.
KU KARANTA : Jigo a MASSOB ya ce Najeriya ta cancanci rabuwa
Ta ci gaba da cewa “zargin da ake ma maigidana siyasa ce ba maganar shari’a ba kamar yadda shugaba Buhari ke son duniya ta dauka. Wannan zalunci da rashin adalci da ake ma maigidana da wasu mutane shi ya jaza kirkiro Neja Delta Avengers (NDA) wadanda ke kiran a saki maigidana abin da shugaba Buhari ke wasa da shi. Ya kamata yana cikin wadanda ake tattaunawa da su, kuma ina son shugaba Buhari ya tuntubi F.W. de Klerk na Afrika ta kudu kan yanda ake tattaunawa da masu neman ‘yanci”
The post Matar Kanu ta soki shugaba Buhari appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Nigerian newspapers 24/7.