SABO: Yan kungiyar Boko Haram sun sace mata 16
– Wani sabon rahoto ta bayyana wanda wasu yan ta’addan Boko Haram sun kama mata 16 a Madagali a jihar Adamawa
– Da wuri ne jita jita daga yan jarida ta nuna cewa wanda wani tsohon shugaban kungiyar Boko Haram mai suna Abubakar Shekau bai mutu ba
– A wani bidiyo wanda ta fito a yau Alhamis 24, ga watan Maris ta nuna bayyana wanda wani mai mutuwa yake maganta kan ci gaba da kungiyar shi
Yan kungiyar Boko Haram a Arewa Maso Ganashin Najeriya
Jaridar Rariya ta ruwaito wanda, yan kungiyar Boko Haram sun sace mata 16 a garin Madagali a jiahr Adamawa, a Arewa Maso Gabashin Najeriya.
KU KARANTA KUMA: Gwamnati zata gana da Fulani makiyaya da Manoma
Rariya ta ci gaba wanda, wasu da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne a jiya Laraba sun sun sace mata 16 a wani kauye da ake kira Sabongari dake garin Madagali a jihar Adamawa. Wasu mazauna yankin sun bayyanawa majiyarmu ta Daily Trust cewa matan sun je kamun kifi ne a rafin Magar tare da rakiyar wasu matasa a lokacin da wasu matasa kusan su takwas rike da bindigu suka yi awon gaba da su.
Matasa biyun da suka raka matan sun tsira inda dayan ya tsira da harbin harsashi, yayin biyu daga cikin matan su ma suka tsira inda suka dawo kauyen. Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Othman Abubakar ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya kara da cewa sun aika da dakarunsu yankin.
Dan majalisa mai wakiltar mazabar Michika da Madagali a majalisar wakilai ta tarayya, Adamu Kamale ya koka kan yadda jami’an tsaro suka yi karanci a wasu kayyukan da ke garin na Madagali.
The post SABO: Yan kungiyar Boko Haram sun sace mata 16 appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read on NAIJ.COM.