Boko Haram: 6 sun mutu, 30 sun raunata inda mata kunar bakin wake sun kai hari
– Wata mata kunar bakin wake sun kari hari a wani kauye mai suna Nguetchewe a iyakar yankin Arewacin kasar Kamaru
– Mutane 6 sun mutu inda yan kauyen sama da 30 sun raunata
– Wani bayani daga hukumar yan sanda ta bayyana wanda akwai yara da yawa tsakanin wadanda sun rasu da samu rauni
Yan ta’addan Boko Haram a kasar Kamaru
A yau Laraba 10, ga watan Faburairu ne mutane sama da 6 sun rasu a kunar bakin wake na biyu a kauyen Nguetchewe, wani gari tsakanin iyakar kasar Najeriya, Jaridar The Punch ta ruwaito.
Wani labari daga masu tsaro ta gaya ma jaridar AFP wanda “mata kunar bakin wake 2 sun tashi kansu da bam a daidai karfe 6:20 da safe inda mutanen a kauyen suka shirya abincin su.”
Wani dan sanda ya bayyana wanda tsakanin mutanen 30 da 50 sun raunata a hare haren inda yaro da matasa da yawa suka cikin wadanda sun raunata.
An dauki wadanda sun samu rauni da yawa zuwa wani Asibiti a garin Maroua.
Idan ba za ku manta ba, a kwanan nan watanni ne wadanda aka zargin yan ta’addan Boko Haram sun kai hari a kasar Kamaru.
A ranar Litinin 25, ga watan Janairu ne yan kunar bakin wake 4 sun kai hari a wani kauye a yankin Arewacin kasar Najeriya inda suka kashe yan kauyen 25.
Sannan, bayan sauran kwanaki bayan hare haren, yan kunar bakin wake 2 sun tashi bama bamai inda mutane 4 sun rasu da kuma sama da 12 sun raunata a gari mai suna Kerawa a Kasar Kamaru.
The post Boko Haram: 6 sun mutu, 30 sun raunata inda mata kunar bakin wake sun kai hari appeared first on Nigeria News today & Breaking news | Read on NAIJ.COM.